Matakan Samun Abinci A Kan Farashi Mai Rahusa A Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Matakan Samun Abinci A Kan Farashi Mai Rahusa A Najeriya
Jan 24, 2025
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Wadatar da al’umma da abinci abu ne mai matukar muhimmanci ga duk ƙasar dake son zama lafiya cigaba.
Sai dai a Najeriya cimma wannan buri na cin karo da ƙalubale, kama daga sauyin yanayi zuwa ambaliyar ruwa, daga rashin tsaro zuwa karancin zuba jari a bangaren noma.

Rahotanni sun nuna cewa adadin abincin da aka samar bai kai yadda ya kamata a ce an samu ba ta dalilin wadannan matsaloli.
Ko me ya kamata a yi don shawo kan wannan mi’ara koma baya da harkar samar da abinci take yi a Najeriya?

Wannan shi ne batun da aka duba yayain Taron Muhawara na Shekara-Shekara na Daily Trust nab ana, kuma a kansa shirin Najeriya a Yau za iyi tsokaci.