Mutanen dake da sha’awar shiga harkar noma kodai don sama wa kansu abin da za su ci ko kuma don samun kudaden shiga na fuskantar kalubale.
Wannan kalubale ya hada da karancin ilimin noman, da na irin shuka, da rashin gonaki da dai sauran su.
Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wannan batu tare da samar da hanyoyin noma ba tare da kashe kudi masu yawa ba.