Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Kasa Kiranye

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Kasa Kiranye
Mar 25, 2025
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Mulkin demokradiyya kamar yadda Hausawa ke cewa ‘yancin dan adam.
A lokacin da ta baka damar tsayawa don a zabe ka kan wani mukami, kazalika ta baka damar zaben wanda kake so ya shugabance ka kuma ya wakilce ka.


Wani abun da demokradiyyar ta baiwa alumma dama a kai kuma shine na yin kiranye ga wakilan da suka zaba musamman idan wadannan wakilan basa biya musu bukatun da suka tura su a kai.
Tuni dai alummar kogi ta tsakiya suka fara kada kuri’un kiranye ga sanatar da suka aike ga majalisar dattawa bisa dalilai nasu na kashin kan su.


Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai tattauna ne kan matakai da sharuddan da ake cikawa don yin kiranye ga ‘yan majalisa.