“Dalilan Da Suka Sa Muke Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyya Mai Mulki”

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
“Dalilan Da Suka Sa Muke Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyya Mai Mulki”
Apr 28, 2025
Idris Ɗaiyab Bature

Send us Fan Mail

Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya shekar da ’yan siyasa daga banarori daban-daban suke yi.


A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa jam’iyyar APC mai mulki ta jawo diga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaben 2027.

Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan Najeriya suke kokawa da yadda ake gudanar da mulki a kasa da yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.


Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci za iyi nazari a kai da nufin gano alkiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.