Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, daya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan kasar.
Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi – shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ka iya haddasawa a rayuwar talaka?
A kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.