Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
May 01, 2025
Idris Daiyab Bature

Send us a text

Cututtuka da dama suna Kamari a Najeriya wanda a mafi yawancin lokuta ma wadanda ke dauke da irin wadannan cututtukan basu da masaniyar suna dauke da su.


 Kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana, zaman lafiya, rashin matsalar kwakwalwa, da samun wadata na daga cikin abubuwan dake tabbatar da lafiyar bil’adama.


 Wata cuta da ta addabi da yawa daga cikin al’umma itace cutar Hawan jini wacce take daya daga cututtuakan dake sanadiyyar mutuwar akalla mutum miliyan biyu a duk shekara a Najeriya.