Tasirin Dangantaka Tsakanin Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Tasirin Dangantaka Tsakanin Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
May 26, 2025
Idris Ɗaiyab Bature

Send us a text

A tsarin mulkin dimokuraɗiyya, dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisun dokoki tana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da shugabanci a tsakanin al’umma.


A galibin kasashe masu bin tsarin na dimokuraɗiyya, ’yan majalisa kan kasance masu wakiltar al’umma da kare muradunta, da sa ido da kuma bayar da shawarwarin da suka dace ga bangaren zartarwa domin ci gaban kasa.
Sai dai a Najeriya, a wasu lokutan akan zargi ’yan majalisa da zama ’yan amshin Shata.
Ko me ya sa haka? Shin yaya ya kamata dangantaka ta kasance a tsakanin banaren zartarwa da majalisar dokoki a tsarin mulkin dimokuraɗiyya?


Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.