Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
Jun 20, 2025
Idris Daiyab Bature

Send us a text

’Yan Najeriya da dama ne dai da suka yi ilimin zamani dole ta sa suka rungumi sana’o’in da a baya ake ganin na kaskantattu ne don su samu na sakawa a bakin salati.


 Mai yiwuwa hakan ne ya sa wasu, musamman matasa, suka yanke kauna da cewa shafe lokaci ana karatun kan iya taimaka wa mutum magance bukatunsa nay au da kullum. 


Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.