Yadda Masu Yi Wa Kasa Hidima Za Su Ci Arzikin Yankunan Da Suke AIki

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Masu Yi Wa Kasa Hidima Za Su Ci Arzikin Yankunan Da Suke AIki
Jul 25, 2025
Idris Daiyab Bature

Send us a text

Bayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati.


Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala.


Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan da aka tura su.