Dalilan Karuwar Mace-Mace A Hanyoyin Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Dalilan Karuwar Mace-Mace A Hanyoyin Najeriya
Aug 14, 2025
Idris Daiyab Bature

Send us Fan Mail

Duk da kara wayar da direbobi da fasinjoji da hukumar kiyaye hadura ta tace tana yi, ana kara samun hauhawar wadanda ke rasa rayukansu sakamakon haddura a titin kasar nan.


A shafinta na internet, hukumar kiyaye haddura ta kasa tace a watanni uku na farko na shekarar 2024, mutane 1,471 ne suka rasa rayukansu sakamakon hatsarin mota, kazalika, a watanni uku na farko na wannan shekara ta 2025, adadin ya haura zuwa mutane 1,593 — karin mutum 122, ko kuma kashi 8.3 cikin dari.


Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ake kara samun karuwa rasa rayuka a titunan kasar nan.