Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu
Nov 21, 2025
Idris Daiyab Bature

Send us Fan Mail

Hukuncin da kotun tarayya ta Abuja ta yanke wa shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB, Mazi Nnamdi Kanu, ya sake tayar da kura a tsakanin magoya bayansa, ‘yan yankin Kudu maso Gabas, da al’ummar Najeriya gaba ɗaya. 


Yayin da gwamnati ke cewa hukuncin ya biyo bayan dogon shari’a da hujjoji da suka tabbatar da aikata laifukan da ake tuhumarsa da su, wasu na ganin batun na da matuƙar sarkakiya musamman ma yadda iyalansa da magoya bayansa ke kallon wannan hukunci.


Shin ko yaya ‘yan uwan Nnamdi Kanu suka kalli wannan hukunci?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.