Halayen Da Ya Kamata Mutum Ya Mallaka Kafin A Nada Shi Jakada

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Halayen Da Ya Kamata Mutum Ya Mallaka Kafin A Nada Shi Jakada
Dec 01, 2025
Idris Daiyab Bature

Send us Fan Mail

A mafi yawan ƙasashen duniya, ana ɗaukar jakadu a matsayin fuskar ƙasa kuma ginshiƙan hulɗar diflomasiyya. Saboda haka, akwai muhimman halaye da suke tilas jakadan ƙwarai ya mallaka domin ya wakilci ƙasarsa cikin mutunci, da nagarta da kwarewa. 


Tun bayan da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fitar da sunayen jakadu da yake sa ran majalisar kasa ta tantance ne dai batun ke ta shan suka daga manazarta kan sunayen da ya fitar.


Ko wadanne irin halaye ya kamata jakada ya mallaka a yayin da za a tura shi a matsayin wakili a wata kasa?


Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.