Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji
Apr 28, 2026
Idris Daiyab Bature

Send us Fan Mail

A kwanakin nan ana samun raguwar kujerun maniyyata aikin Hajji daga Najeriya, abin da ya jawo fargaba ga masu shirin zuwa kasa mai tsarki da kuma masu hidimar su. 

 

A da, Najeriya na samun kujeru sama da dubu casa’in daga gwamnatin Saudiyya, amma cikin shekaru kadan da suka gabata adadin ya ragu zuwa kusan dubu sittin da biyar. 

Ko yaya kara raguwar kujerun maniyyatan Najeriya ke kara tasiri ga Najeriya?


Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi duba a kai.