Daga Laraba

Abin Da Ya Sa Kotu Ta Tsige Gwamnonin Arewa Huɗu

Aminiya

Bayan watanni tara da kammala zaben 2023 da zubar da wasu jiga-jigan yan siyasa, bangaren shari’a ma na cigaba da zartar da hukunci, inda zuwa yanzu aka tsige akalla gwamnoni hudu daga jam’iyyu daban-daban.

Wasu na ɗiga ayar tambaya kan saƙaƙiyar da alƙalai ke amfani da su wajen yanke hukunci a kotunan.

Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba ainihin dalilan da suka sa kotunan tsige gwamnonin huɗu zuwa yanzu.