
Daga Laraba
Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.
Episodes
212 episodes
June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
An ayyana 12 ga watan Yunin kowace shekara a matsayin Ranar Dimokuradiyya a Najeriya don tunawa da ranar da aka gudanar da zaben da aka yi amanna cewa shi ne mafi sahihanci da inganci a tarihi.Sai dai bayan fiye da shekara 30 da wann...
•
27:38

Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami'an Kiwon Lafiya
Asibiti ko dakin shan magani ko wani bigire mai kama da wadannan wuri ne da marasa lafiya kan je ko ake kai su don neman waraka a duk lokacin da bukatar haka ta taso.Wuri ne da akan ware domin ceto rayukan wadanda suka jikkata suke k...
•
26:28

Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah
Yayin da sallah ya gabato, mutane da dama kan yi fadi tashi don biyan wasu bukatun su na bukukuwan sallah, kuma kamar yadda aka saba, a irin wannan lokaci ne iyalai da dama kan maida hankulan su don ganin sun biya wasu daga cikin bukatun su mus...
•
25:44

“Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”
Rashin iya siyan audugar Alada ga mata na kara jefa su cikin matsaloli da dama, a wasu lokuta ma har da cututtuka da ka iya jawo musu matsaloli.A cewar wani rahoto da Asusun yara na majalisar dinkin duniya UNICEF da WaterAid n...
•
24:22

"Abba Al'mustafa Bashi Da Hurumin Dakatar Da Fina Finan Mu"
Dangantaka na kara runcabewa tsakanin Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano, wato Kano State Censorship Board, hukumar da aka kafa a shekarar 2001 domin kula da tsaftar fina-finai da nishaɗi a jihar, musamman a fannin kiyaye al’ada da koyarwar ...
•
27:06

Tasirin Mulkin Karba-Karba A Najeriya
Karba-karba wani tsari ne da ya tanadi kewayarwar ludayi a tsakanin kudanci da arewacin Najeriya wajen rike shugabancin kasa. Manufar tsarin, wanda babu shi a Kundin Dokokin Najeriya, ita ce tabbatar da daidaito da haɗin kai da ...
•
26:48

Boyayyun Dalilan Da Suke Sa Faduwa Jarabawa A Najeriya
Duk shekara, dalibai kan rubuta jarabawa a matakai daban-daban na makarantu daban-daban.Daya daga cikin nau’ukan jarabawa da daliban Najeriya suke yi ita ce Jarabawar Sharen Fagen Shiga Manyan Makarantu, wato UTME.Kamar kowace...
•
23:18

Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
Tatsuniya wata hanya ce ta ilmantarwa da bayar da tarbiyya da kuma koyar da al’adu da halaye na gari a tsakanin Hausawa.Tatsuniyoyi na ɗauke da darussa na rayuwa, suna kuma koya wa yara da manya jarumta da tausayi da sauran dabi’u ky...
•
30:56

Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
Wutar lantarki ta zama tamkar gwal a wasu sassan Arewacin Najeriya, inda a wasu yankuna aka ba da rahoton samun sa’o’i biyu kawai a rana, wasu kuma ba sa samun ko daidai da dakika daya.Masu kananan sana’o’i suna kallon rayuwarsu da k...
•
26:11

Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo
Duk wanda aka haifa ya tashi a kasar Hausa ya san al’adar nan ta bayar da ko karɓo ɗa ko ‘ya riƙo. A wasu lokutan mutum ne ke nema a ba shi rikon, a wasu lokuta kuma iyayen ne suke bayarwa don ƙashin kansu.Wannan alada ana yin ...
•
23:01

Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’
Tun kaka da kakanni an san Hausawa da kawaici da kunya da kuma girmama na gaba da su.Mai yiwuwa wadannan dabi’u ne suka sa matar Bahaushe ba ta iya hada ido da mijinta, balle ta kira shi da sunansa na yanka.To amma a zamani...
•
23:51

Dalilan Zuwan Mafarautan Arewa Kudancin Kasar Nan
Tun bayan kisan mafarauta 16 dake hanyar su ta dawowa gida a garin Uromi dake karamar hukumar Esan dake jihar Edo ne dai al’umma da dama ke ta aikewa da sakon alhini ga ‘yan uwa da abokan arziki yayin da wasu kuma ke ta neman amsoshin tambayoyi...
•
30:11

Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah
A duk lokacin da aka ce lokutan bukukuwa sun karato, akan samu sauyi a dukkan alamura.Daya daga cikin irin wadannan sauyi da ake samu shine na farashin kayayyakin masarufi. A wasu lokuta, akan samu tashin farashin ...
•
26:36

Abin Da Kundin Tsarin Mulki Ya Ce A Kan Ayyana Dokar Ta Ɓaci
A karshe dai hasashen da wasu ke yi a Ribas ya tabbata, inda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci, ya dakatar da zababben gwamnan da mataimakiyarsa, da ma ''yan majalisar dokokin jihar.Sai dai bayan ayyana wannan d...
•
27:18

Ko Kun San Asalin Tashe Da Tarihinsa A Kasar Hausa?
Bayan dunbum falala, da yawan samuwar ibadun dake kara kusanta bayi ga ubangijin su, da azumin watan ramadana ke zuwa dashi kamar yadda malamai suka saba fada mana, Hakazalika Kuma a watan na Ramadan dai na zuwa da wata alada mai dimbin tarihi ...
•
27:42

Yadda Zawarawa Suke Dandana Kuda A Watan Ramadana
Kowane Musulmi da yadda yakan shiga watan Ramadana – wani kan shiga da shiri, wani kuma da shiririta.Sai dai wasu watan kan zo musu da kalubale – ba don sun shirya mishi b aba kuma don sun gaza shiryawa.Wani rukunin wadannan muta...
•
31:09

Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa
A duk lokacin da aka ɗaura aure, wata addu’a da ’yan uwa da abokan arziki kan yi ita ce “Allah Ya kawo ƙazantar ɗaki”.A al’adance, ɗaya daga cikin manyan dalilan yin aure shi ne samun haihuwa. Sai dai a wasu lokuta, wasu maz...
•
23:12

Me Ya Sa ’Yan Najeriya Suke Buga-Buga Ko Da Suna Aikin Albashi?
Yanayin tattalin arziki da ma wasu dalilai kan tilasta wa mutane da dama, ciki har da masu karbar albashi a karshen wata, neman wata hanya ta daban dake kawo Karin kudade.Shin mene ne yake kawo hakan, kuma mene ne tasirinsa a kan rayuwa...
•
22:33

Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa
Zanen fuska na da dadadden tarihi a Arewacin Najeriya musamman a kasar Hausa.Sai dai wannan dadaddiyar al’ada tana kan hanyar gushewa domin kuwa ba kasafai ake samun wadanda suke yin ta a wannan zamani ba.Shirin Daga Larab...
•
29:44

Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma 'Event Centre'
A da akan kwashe kwanaki ana bukuwan aure a kasar Hausa, kama daga kamu, zuwa sa lalle, yinin bik da zaman ajo zuwa budar kai da sayen baki.Sai dai wadannan al’adu sannu a hankali suna ta gushewa.Ko mene ne dalilin wannan sauyin?...
•
29:48

Dalilan Da Suka Sa Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata
Son haihuwar ‘ya’ya maza fiye da ‘ya’ya mata abu ne da ake samu tun tale-tale a tsakanin alummomi daban-daban.A tsakanin wasu al’ummomin, samun da namiji abin alfahari ne wanda kuma yake nuni da cigaba da dorewar ahali; sai dai ba a cik...
•
29:49

Me Ya Sa Matasa Ba Sa Ɗaukar Koyarwa A Matsayin Sana'a?
Samun ingattattun malamai a makarantun firamare da sakandare na taka muhimmiyar rawa wajen samar da tubalin ingantaccen kuma nagartaccen ilimi a cikin al’umma.Ɗorewar wannan fafutuka ta samar da ingantaccen ilimi kuma ta dogara ne a kan...
•
26:56

Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo
Duk wanda aka haifa ya tashi a kasar Hausa ya san al’adar nan ta bayar da ko karɓo ɗa ko 'ya riƙo. A wasu lokutan mutum ne ke nema a ba shi rikon, a wasu lokuta kuma iyayen ne suke bayarwa don ƙashin kansu.Wannan alada ana yin ...
•
23:01
