 
  Daga Laraba
Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.
Episodes
231 episodes
    Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya
Sabuwar dambarwa ta kunno kai tsakanin wasu manyan ‘ya’yan jam’iyyar adawa ta PDP, inda ake zargin cewa rikicin ya kai ga hana tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, sayen fom ɗin takarar shugabancin jam’iyyar.Rahotanni sun nun...
        
          
          •
          27:19
        
       
    Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?
Yadda ‘ya’yan jamiyyar PDP ke ficewa suna komawa jam’iyya mai mulki na cigaba da nuna yadda take kara samun koma baya a siyasar Najeriya.Banda haka, rikicin cikin gida da yaki ci yaki cinyewa na cigaba da yi mata dabaibayi.
        
          
          •
          27:17
        
       
    Yadda Aka Yi Almajiri Ya Zama Mabaraci
A zamanin nan, ana alakanta almajirai da bara – hasali ma a lokuta da dama akan yi amfani da kalmar “almajiri” idan ana nufin mabaraci.  Amma a da ba haka lamarin yake ba – almajiri baya bukatar yin bara ko roko kafin y...
        
          
          •
          29:35
        
       
    Tasirin Bambance-bambance Tsakanin ‘Yan Najeriya Shekara 65 Da Samun ‘Yancin Kai
Tun daga ranar 1 ga Oktoba, 1960, Najeriya ta samu ’yancin kai daga Turawan mulkin mallaka. Amma tun daga wannan lokaci, al’ummar Najeriya sun kasance cike da bambance-bambancen addini da kabila da harshe da al’adu da kuma ra’ayin siyasa. Wadan...
        
          
          •
          30:16
        
       
    Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
Duk da amfanin kifi ga lafiyar jikin mutum da kuma samar da kudin shiga masana sun ce ba a amfani da shi yadda ya kamata a Najeriya. Baya ga bai wa jiki lafiya, kifi  ka iya samar da kudaden shiga ga daidaikun ’yan Najer...
        
          
          •
          27:52
        
       
    Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani. Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’a...
        
          
          •
          29:45
        
       
    Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku
Sau da dama mukan ji labarai na mutane da suka ɗauki rayukansu saboda damuwa, talauci ko kuma rashin samun mafita a cikin rayuwa. A cikin wannan shirin, za mu kalli batun kisan kai daga wani ɓangare na daban, ba wai kawai...
        
          
          •
          27:39
        
       
    Hare-hare Kan Tarurrukan Siyasa Da Alakarsu da 2027
Karuwar hare-hare kan ’yan siyasa a kwanan nan ta sa wasu ’yan Najeriya sun fara fargabar abin da ka iya faruwa idan aka fara yakin neman zaben 2027.A kwanan nan ne dai wasu wadanda ake zargin ’yan bangar siyasa ne suka kai hare-hare...
        
          
          •
          21:20
        
       
    Yadda Mata Dake Auren Gwaji Suke Yamutsa Hazo
Wani sabon salo da wannan zamani ya zo da shi shi ne auren gwaji, inda mata kan yi shiga gidan miji da niyyar fita bayan wani lokaci.Sai dai manazarta suna cewa hakan ka iya haddasa matsalolin musamman idan mazajen auren ba su san da...
        
          
          •
          28:31
        
       
    Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa
A duk lokacin da aka ɗaura aure, wata addu’a da ’yan uwa da abokan arziki kan yi ita ce “Allah Ya kawo ƙazantar ɗaki”. A al’adance, ɗaya daga cikin manyan dalilan yin aure shi ne samun haihuwa.  Sai dai a wasu loku...
        
          
          •
          23:12
        
       
    Yadda wasu tsare-tsaren ba da tazarar haihuwa ke yin illa ga mata
A kokarin iyaye mata na kula da lafiyarsu da kuma tsare lafiyar iyalansu, hanyoyin bada tazarar haihuwa na asibiti sun zama zabin da dama ke komawa gare su. Sai dai duk da shaharar wadannan hanyoyi, akwai mata da dama da ...
        
          
          •
          27:02
        
       
    Yadda Sinadaran Dandanon Abinci Ke Yin Illa Ga Lafiya
A yau, yawancin mutane suna amfani da sinadaran dandano wajen girki domin ƙara wa abinci ɗanɗano da ƙamshi. Amma, binciken masana ya nuna cewa ana yawan amfani da su fiye da yadda ake bukata, musamman irin waɗanda aka sarrafa a masana’antu....
        
          
          •
          26:09
        
       
    Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani?
Wasu matasa sun zabi tallata ‘yan siyasa a kafafen sada zumunta na zamani ta yadda bai kamata ba a wasu lokutan.Tallata ‘yan siyasa da matasan suke yi kan haifar da hatsaniya, ko kiyayya, a intanet ko ma a zahiri a tsakanin su.
        
          
          •
          29:16
        
       
    Dalilan Alummomi Na Rungumar Gwaji Kafin Aure
Wasu alummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi gwajin ma’aurata kafin a daura musu aure.A wasu lokutan akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure da suka hada da yaduwar cutuka,...
        
          
          •
          25:56
        
       
    Abubuwan Da Ya Kamata Yara Su Yi Yayin Hutun Makaranta
A duk lokacin da akace an kammala zangon karatu, dalibai kan samu hutu don hutawa da yin wadansu abu na dabam da kuma basu damar shakuwa da ‘yan uwa da abokan arziki.Kamar yadda masana harkar masana harkar ilimi suka saba fadi...
        
          
          •
          28:45
        
       
    Makomar Siyasar Najeriya Bayan Rasuwar Shugaba Buhari
Masana da masu sharhi suna ganin cewa rasuwar shugaba Muhammadu Buhari ta haifar da babban gibi a siyasar Najeriya, musamman a Arewa.Wasu ma suna ganin rasuwar Buhari ka iya kawo tasgaro ga jamiyya mai Mulki, wadda take ganin ...
        
          
          •
          24:18
        
       
    Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
Mai yiwuwa masu sauraro sun san wani bawan Allah wanda kusan a kullum, kuksan a ko yaushe a cikin nema yake, amma Allah bai kawo ba..Wasu dai na ganin yawan fadi-tashin da mutum yakan yi ba shi ne zai ba shi kudaden da yake bukata ba...
        
          
          •
          19:29
        
       
    Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa
Burodi ya zama daya daga cikin abincin da ‘yan Najeriya basa iya yi babu shi. Yayin da wasu ke cin shi a matsayin abin Karin kumallo da safe, wasu kuwa na cin shi a matsayin abincin rana a wasu lokutan ma har da na dare.A duk ...
        
          
          •
          29:21
        
       
    Shin Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
Hare haren ‘yan ta’adda na kara ta’azzara a yankuna daban daban na fadin kasar nan wanda hakan ke nuni da Karin rashin tsaro da ya dade yana ciwa alumma da ma gwamnati tuwo a kwarya.Ko a kwana kwanan nan an ga yadda jihar fila...
        
          
          •
          28:33
        
       
    June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
An ayyana 12 ga watan Yunin kowace shekara a matsayin Ranar Dimokuradiyya a Najeriya don tunawa da ranar da aka gudanar da zaben da aka yi amanna cewa shi ne mafi sahihanci da inganci a tarihi.Sai dai bayan fiye da shekara 30 da wann...
        
          
          •
          27:38
        
       
    Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami'an Kiwon Lafiya
Asibiti ko dakin shan magani ko wani bigire mai kama da wadannan wuri ne da marasa lafiya kan je ko ake kai su don neman waraka a duk lokacin da bukatar haka ta taso.Wuri ne da akan ware domin ceto rayukan wadanda suka jikkata suke k...
        
          
          •
          26:28
        
       
    Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah
Yayin da sallah ya gabato, mutane da dama kan yi fadi tashi don biyan wasu bukatun su na bukukuwan sallah, kuma kamar yadda aka saba, a irin wannan lokaci ne iyalai da dama kan maida hankulan su don ganin sun biya wasu daga cikin bukatun su mus...
        
          
          •
          25:44
        
       
    “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”
Rashin iya siyan audugar Alada ga mata na kara jefa su cikin matsaloli da dama, a wasu lokuta ma har da cututtuka da ka iya jawo musu matsaloli.A cewar wani rahoto da Asusun yara na majalisar dinkin duniya UNICEF da WaterAid n...
        
          
          •
          24:22
        
       
    "Abba Al'mustafa Bashi Da Hurumin Dakatar Da Fina Finan Mu"
Dangantaka na kara runcabewa tsakanin Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano, wato Kano State Censorship Board, hukumar da aka kafa a shekarar 2001 domin kula da tsaftar fina-finai da nishaɗi a jihar, musamman a fannin kiyaye al’ada da koyarwar ...
        
          
          •
          27:06
        
      