Daga Laraba

Yadda Shara Ke Neman Binne Manyan Biranen Najeriya

Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Use Left/Right to seek, Home/End to jump to start or end. Hold shift to jump forward or backward.

0:00 | 27:44

Tururuwar da mutane suke yi zuwa manyan biranen Najeriya na  barazana ga  wadannan alƙaryu ta fuskar tsaftar muhalli.

Misali, wani rahoto da Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa a duk sa'a daya  birnin Legas kan yi baƙi 77 – hakan kuma kan haddasa karuwar sharar da ake zubarwa.

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan yadda shara ke addabar wasu manyan biranen Najeriya da tasirinta a kan lafiyar jiki da ta muhalli.