
Daga Laraba
Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.
Daga Laraba
Boyayyun Dalilan Da Suke Sa Faduwa Jarabawa A Najeriya
Duk shekara, dalibai kan rubuta jarabawa a matakai daban-daban na makarantu daban-daban.
Daya daga cikin nau’ukan jarabawa da daliban Najeriya suke yi ita ce Jarabawar Sharen Fagen Shiga Manyan Makarantu, wato UTME.
Kamar kowace shekara, a bana ma dalibai sun rubuta wannan jarabawa kuma a cewar Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB), kashi 78.5 cikin 100 na wadanda suka rubuta jarabawar sun samu kasa da maki 200.
Ko wadanne dalilai ne suke kawo faduwa jarabawa a Najeriya?
Wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi kokarin amsawa.