Daga Laraba

Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?

Idris Daiyab Bature

Yadda ‘ya’yan jamiyyar PDP ke ficewa suna komawa jam’iyya mai mulki na cigaba da nuna yadda take kara samun koma baya a siyasar Najeriya.


Banda haka, rikicin cikin gida da yaki ci yaki cinyewa na cigaba da yi mata dabaibayi.

Shin ko hakan na nufin jam’iyyar ta fara gushewa ne a siyasar Najeriya?


Wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari a kai.