Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Gudummawar Da Kowa Zai Bayar Wa Wurin Kawar Da Ta'addanci
•
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed
Zuwa yanzu ya fara zama zahiri a idanun duniya cewa Najeriya ta fada cikin taskun rashin tsaro da kullum yake mata barazanar cigaba da kasancewar ta kasa dunkulalliya mai shugabancin da ake yi wa biyayya.
Tuni dai kasar ta ayyana kungiyoyin yan bindiga guda biyar a matsayin 'yan ta'adda. Hudu daga cikinsu a Arewacin kasar daya a Kudancin ta.
To ko ta wadanne hanyoyi 'yan kasar za su hada kai da gwamnati domin ceto kansu da kasar su?
Ayi sauraro lafiya.