Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Episodes
924 episodes
Tasirin Yankan Al’aura A Rayuwar 'Ya'ya Mata
A tsakanin al’ummomi daban-daban akan samu wasu al’adu na yanke wani bangare na al’aurar ’ya’ya mata saboda wasu dalilai.A kasar Hausa akan yi abin da ake kira yankan angurya da nufin rage wa mace sha’awa, musamman kafin ta yi...
•
25:44
Hanyoyin Mallakar Gida Ga Mai Karamin Karfi
Mallakar muhalli na cikin burace-buracen kusan kowanne dan Najeriya.Sai dai wadannan burace-burace, a galibin lokuta, ba sa cika – musamman ga masu matsakaitan samu.Amma wasu masana suna ganin akwai dabarun da marasa karfi ma za s...
•
24:47
Abin Da Ya Kamata Ku Yi Yayin Takaddama Da ’Yan Sanda
Babban alhakin da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya dora wa Rundunar ’Yan Sanda shi ne kare rayuka da dukiyoyin ’yan kasa. Sai dai a lokuta da dama, akan samu fito-na-fito sakamakon zargin ’yan sanda da wuce gona da iri wajen gudanar...
•
20:08
Rayuwar Mazan Da Ba Sa Haihuwa
Rashin haihuwa matsala ce da ka iya wargaza gidajen aure musamman a wannan zamani.Da an samu shekara biyu zuwa uku bayan an daura aure ba tare da an samu karuwa ba za a fara yamadidi da matar a kan ba ta haihuwa.Sai dai likitoci s...
•
21:40
Inda Aka Mike Da Inda Aka Kauce Tun Bayan Dawowa Mulkin Dimokuraɗiyya A Jamhuriya Ta Hudu
Kamfanin yaɗa labarai na Media Trust ya daɗe yana taka muhimmiyar rawa wajen buɗe tattaunawa masu ma’ana kan manyan al’amuran da suka shafi tafiyar da ƙasa da dimokuraɗiyya a Najeriya. Daga cikin fitattun shirye-shiryensa akwai muhawarar shekar...
•
15:09
Nasarori Da Kalubalen Da Bankin Musulunci ke Fuskanta A Najeriya
A Jamhuriya ta Hudu a Najeriya, wadda ta fara a shekarar 1999, an samu sauye-sauye masu yawa a bangaren tattalin arziki da harkokin kuɗi, ciki har da tasowar bankunan Musulunci. Wannan tsari na banki ya samo asali ne daga buƙatar samar da hanyo...
•
25:15
Tasirin Siyasar Matasa A Najeriya Tun Bayan Dawowar Jamhuriya Ta Hudu
Shekaru kafin a sanya hannu kan dokar Not Too Young To Run, siyasar matasa a Najeriya na fuskantar ƙalubale masu tarin yawa. Duk da cewa matasa su ne mafi rinjaye a yawan al’umma da kuma masu katin zaɓe, an dade ana kallonsu ne a matsayi...
•
19:57
Yadda Siyasar Ubangida Ta Yi Tasiri Ga Siyasar Najeriya A Jamhuriya Ta Hudu
Tun bayan dawowar mulkin farar hula a shekarar 1999, siyasar Najeriya ta kasance karkashin inuwar wasu ’yan tsiraru da ake kira iyayen gidan siyasa. Wannan tsari ya ginu ne a kan karfin mutum guda ko rukuni, inda su ke rike da makullin jam’iyya...
•
25:06
Abun Koyin ‘Yan Siyasa Da Matasa Kan Jarumtar Goodluck Jonathan A 2015
Kiran wayan da tsohon Shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan ya yi wa marigayi Muhammadu Buhari ta bar tarihi mai muhimmanci a Najeriya.Waya da ta kwantar da hankalin kasa, ta kuma dakatar da fargabar tashin hankali. A ranar da s...
•
19:09
Bayan Shekaru Sittin, Me Ya Sa Har Yanzu Ake Tunawa Da Su Sardauna?
A tarihin kowace ƙasa, akwai wasu mutane da ba lokaci ko sauyin zamani ke iya gogewa daga ƙwaƙwalwar al’umma ba. A Najeriya, waɗannan su ne founding fathers — jagororin da suka tsaya tsayin daka wajen jagorantar gwagwarmayar neman ’yan...
•
21:37
Zabukan Da Aka Gudanar Lokacin Dawowar Mulkin Farar Hula A Jamhuriya Ta Hudu
Bayan kusan shekaru goma sha shida na mulkin soja, Najeriya ta dawo kan tafarkin mulkin farar hula a shekarar 1999, abin da ya buɗe sabon babi a tarihin siyasar ƙasar. Zaɓen da aka gudanar a wannan lokaci shi ne zaɓen farko na Jamhuriya ta Huɗu...
•
21:52
Waiwaye Kan Yadda Jam’iyyun Siyasa Suka Kafu A Jamhuriya Ta Hudu
Jamhuriya ta Huɗu a Najeriya ta fara ne a ranar 29 ga Mayu, 1999, bayan kawo ƙarshen mulkin soja, inda ƙasar ta koma tafarkin dimokuraɗiyya bisa Kundin Tsarin Mulki na 1999. A wannan lokaci ne aka kafa manyan jam’iyyun siyasa kamar PDP, wadda A...
•
29:28
Lokacin Da Ya Kamata A Fara Yakin Neman Zaben 2027
A siyasar Najeriya, akwai ka’idoji da dokoki da ke tsara yadda ake gudanar da zaɓe, ciki har da lokacin da doka ta amince a fara yaƙin neman zaɓe. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, wato INEC, ita ce ke da alhakin bayyana jadawalin zaɓe da kuma ranar da ‘ya...
•
10:05
Yaya Matsayar Katsalandar Din Da APC Tace Nyesom Wike Na Yi A Jam’iyyar?
A cikin ‘yan kwanakin nan, siyasar Najeriya ta sake daukar sabon salo, bayan barkewar takaddama tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, da manyan shugabannin jam’iyyar (APC). Jam’iyyar APC na kallon yadda Wike — wanda...
•
14:57
Yadda ‘Yan Bindiga Suka Yanka ‘Yan Kasuwa A Jihar Neja
Harin da wasu ‘yan ta’adda suka kai kasuwar Daji da ke karamar hukumar Borgu a Jihar Neja ya sake jawo hankalin al’umma kan matsalar rashin tsaro da ke kara ta’azzara a yankunan karkara na Arewa ta Tsakiya. Kasuwar Daji, wadda ke zama cibiyar h...
•
15:14
Sharuddan Da Jam'iyya Za Ta Cika Kafin Kiran Ta Babban Jam'iyyar Adawa
A fagen siyasar Najeriya a halin yanzu, ana ta ce-ce-ku-ce kan wacce ce babbar jam’iyyar adawa da za ta iya tsayawa ƙafada da ƙafada da jam’iyyar APC mai mulki. Wannan takaddama ta fi karkata ne tsakanin jam’iyyar PDP, wacce ta dade tana taka r...
•
23:04
Yadda Ya Kamata Ku Gudanar Da Rayuwa A Shekarar 2026
Shekarar 2026 ta zo a wani lokaci da ’yan Najeriya da dama ke fuskantar matsin tattalin arziki, da sauye-sauyen siyasa, da kuma ƙalubalen rayuwa da ke bukatar sabon tunani. Wannan ba lokaci ba ne na fatan samun sa’a kawai, lokaci ne na tsara ha...
•
17:00
Siyasa Da Tsare-tsaren Gwamnati Da Suka Dabaibaye 2025
Yayin da muke bankwana da shekarar 2025, siyasar Najeriya ta kasance cike da sauye-sauye, rikice-rikice, da kuma manyan al’amura da suka shafi iko, jam’iyyu da shugabanci. Shekarar ta shaida sauyin sheƙa na ‘yan siyasa, rikicin cikin gida a was...
•
21:38
Waiwaye Kan Manyan Kalubalen Tsaro Da Suka Faru A 2025
A shekarar 2025, Najeriya ta fuskanci manyan ƙalubalen tsaro da suka fi daukar hankali, musamman hare-haren ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, da ta’addanci a jihohin Arewa kamar Zamfara, da Katsina da Sokoto da Kaduna da kuma Borno. Hare-haren s...
•
18:49
Yadda Kiristoci Ke Gudanar Da Bikin Kirsimeti A Cikin Musulmi
A duk faɗin Arewacin Najeriya, ana gudanar da bukukuwan Kirsimeti cikin kwanciyar hankali da fahimtar juna, duk da kasancewar Musulmai ne suka fi rinjaye a yawancin yankuna. Kiristoci kan yi bukukuwansu cikin mutunta al’adar Musulmai, yayin da ...
•
16:33
'Halin Kunci Da Muke Ciki A Sansanin Gudun Hijira Yayin Bikin Kirsimeti'
A yayin da al’ummar Kirista a sassa daban-daban na ƙasar nan ke gudanar da bukukuwan Kirsimeti cikin walwala, da annashuwa da haɗuwa da iyalai, akwai kuma waɗanda wannan lokaci ya zo musu cikin ƙunci da jimami. Waɗannan s...
•
14:01
Yadda Farashin Kayayyaki Suke Gabanin Bukukuwan Kirsimeti
Gabannin bukukuwan Kirsimeti, kasuwanni a sassan ƙasar nan sun cika sun bunkasa. Jama’a na ci gaba da zirga-zirga domin sayen kayan bukukuwa, yayin da ‘yan kasuwa ke kokarin jawo hankalin masu saye ta hanyar daidaita farashi.
•
14:23
Cushe-cushen Da Ake Zargin An Yi A Sabbin Dokokin Haraji
Takaddama mai zafi ta dabaibaye sabbin dokokin haraji da Majalisar Tarayya ta amince da su, bayan zarge-zargen cewa an samu sauye-sauye a cikin dokokin bayan an kammala dukkan matakan amincewa da su a majalisa. Batun da ya taso ya jawo cece-kuc...
•
19:37