Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Episodes
944 episodes
Yadda Matasa Ke Bada Gudunmawar Cigaban Al’ummarsu
Samun matasan dake bada gudunmawa a alummomin da suke rayuwa a cikin ta yana da matukar wuya a wannan zamani. Amma duk da haka, wasu matasa sun sadaukar da rayuwarsu wajen bada gudunmawarsu wajen cigaban alummarsu.&nb...
•
28:24
Yadda Na Rasa 'Ya'ya Na Ga Guban Abinci
Cin guba ta hanyar abinci (food poisoning) wata cuta ce da ke faruwa idan mutum ya ci abinci ko ya sha abin sha da ya gurɓace. Gurɓacewar abincin na iya fitowa daga ƙwayoyin cuta kamar Salmonella, E. coli, ko Listeria, ko kuma daga ƙwayoyin cut...
•
25:47
Daga Alkawari Zuwa Mulki, Yadda Siyasa Ke Sauya Manufa
Duk bayan shekaru hudu, Najeriya na kara yin zabe kuma ko wanne lokaci 'yan takara kan dauki alkawurika.Ko shekaru nawa wadanda ake zabe ke bukata don cika alkawuran da suka dauka?wannan shine batun da shirin...
•
27:00
Abubuwan Da Za Su Kwadaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
Alqurani mai girma a cikin suratul Baqarah Allah ya wajabta wa musulmi da suka cika wasu sharudda azumtar watan Ramadana.Kamar yadda malamai suka sha fadi, wannan wata na dauke da wasu falala maras misaltuwa da bawa kan samu idan ya...
•
24:06
Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?
Ko kun san sunan dabinon da kuka fi so ku ci a lokacin shan ruwa? Dan Agadas ne, ko Ruwa-Ruwa, ko Annakhiyl? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai ya yi nazari ne kan nau’ukan dabino da alfanunsa ga dan’Adam...
•
30:13
Kalubalen Dake Tattare Da Samar Da ‘Yansandan Jihohi A Najeriya
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sha nanata muhimmancin samar da ’yan sandan jihohi a Nigeria, yana mai cewa hakan na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar sassa daban-daban na kasar. Shugaban ya ba...
•
25:43
Yadda Cutar Zazzabin Lassa Ke Kisa Da Hanyoyin dakile Ta
A yayin da Najeriya ke fuskantar kalubale daban-daban a fannin lafiya, cutar zazzabin Lassa ta sake ɗaga kai a wasu jihohin ƙasar. Cutar wadda ake dangantawa da berayen da ke ɗauke da ƙwayar cutar, tana yawaita ne musamman a lokutan sanyi zuwa ...
•
19:44
Yadda Ake Kamuwa Da Basir Da Hanyoyin Magance Ta
Cutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu ...
•
26:06
Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki
Alumma na yin azumi ne bisa dalilan addini don samun lada kamar yadda Allah ya umurta a cikin Qurani mai girma. Sai dai daga baya binciken masana kimiyya ya gano cewa bayan lada da ake samu daga yin azumi, akwai wasu alfanu da m...
•
29:58
Falalar Bude Baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi
Hadisi ya tabbatar da yadda cin abinci tare yake kara dankon zumunci da kaunar juna da albarka a tsakanin al’umma. Mai yiwuwa wannan ne ya sa akan samu Karin kusanci da shakuwa a tsakanin duk iyalan da kan zauna su ci abinci.
•
26:29
Me Nadin Sabon Sufeton 'Yansanda Ke Nufi Ga Tsaron Cikin Gida Najeriya?
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa sabon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP), matakin da ya sake jawo hankalin al’umma kan makomar tsaro da gyaran harkokin rundunar ‘yan sandan ƙasar nan. Naɗin sabon jagoran rundunar ya zo ne a daidai lokac...
•
18:51
Shin Da Gaske An Fara Samun Ɓaraka Tsakanin Atiku Abubakar Da Peter Obi A Tafiyar ADC?
Rahotanni daga sassa daban-daban na siyasar Najeriya na nuna cewa ana fara samun ɓaraka a tsakanin manyan jiga-jigan haɗakar tafiyar ADC, musamman tsakanin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa...
•
20:11
Falalar Sallan Tarawih Ga Alummar Musulmi A Watan Ramadan
A duk lokacin da watan azumin Ramadan ya kama, al’ummar Musulmi kan cika masallatai domin gudanar da sallar Tarawihi cikin karsashi da himma. A kwanakin farko, ana ganin sahu sun cika, zuciya cike da nishadi da kwadayin lada. Sai dai abin takai...
•
17:10
Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
Cututtuka da dama suna Kamari a Najeriya wanda a mafi yawancin lokuta ma wadanda ke dauke da irin wadannan cututtukan basu da masaniyar suna dauke da su. Kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana, zaman lafiya, rashin matsa...
•
24:51
Yadda Masu Larurar Ulcer Za Su Gudanar Da Azumin Ramadan Ba Tare Da Matsala Ba
A duk lokacin da watan azumi ya zo, Musulmai da dama sukan karɓe shi da murna da shauƙi, suna shirya ibada da ƙara kusanci da Allah. Sai dai ga wasu, musamman masu fama da larurar gyambon ciki wato ulcer, watan azumi kan zo da wani yanayi na da...
•
18:14
Yadda Muka Yi Asarar Miliyoyin Naira A Kasuwar Singa Muna Ji Muna Gani
‘Yan kasuwa da dama a jihar Kano sun kwana sun tashi da juyayi da alhinin gobara da ta faru ta kuma lashe musu dimbin dukiyarsu suna ji suna gani ba tare da sun iya tabuka komai ba.Gobarar da ta tashi a kasuwar singa dake jiha...
•
17:21
Ya Kamata Najeriya Ta Samar da Dokoki Kan Amfani da AI?
Tun bayan bayyanar kirkirarrriyar basira wato AI ne dai wasu mutane suke amfani da ita ta hanyar da da bai kamata ba. Wasu sukan yi amfani da ita wajen saka hoto ko kirkirar faifan bidiyo wanda zai nuna wani yana yin abun da bai...
•
25:30
Hanyoyin Magance Laifukan Da Matasa Ke Aikatawa A Cikin Al'umma
Masu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa. In ba haka ba, me ya kai matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka ofishin ’yan sanda, suka kuma fit oba tare da wani ya harae su ko ya yi mutsu tsawa ba, balle ya saka su a ce...
•
24:44
Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Samun Wadataccen Abinci
A wannan zamani, ’yan Najeriya da dama ba sa samun wadataccen abinci a yini.Magidanta da dama, musamman, sun tsallake sun bar iyalansu sun shiga bariki don neman na sanyawa a bakin salati. Mene ...
•
25:59
Dabarun Bunkasa Kasuwanci A Intanet
Masu iya magana kan ce “zamani riga”.Sauyin zamani ya kawo sauye-sauye da dama a yadda ake gudanar da harkoki, ciki har da kasuwanci.A yanzu haka, zamani, intanet na taka muhimmiyar rawa wajen tallata haja ko saye da sayarwa.<...
•
27:23
Tasirin Yankan Al’aura A Rayuwar 'Ya'ya Mata
A tsakanin al’ummomi daban-daban akan samu wasu al’adu na yanke wani bangare na al’aurar ’ya’ya mata saboda wasu dalilai.A kasar Hausa akan yi abin da ake kira yankan angurya da nufin rage wa mace sha’awa, musamman kafin ta yi...
•
25:44
Hanyoyin Mallakar Gida Ga Mai Karamin Karfi
Mallakar muhalli na cikin burace-buracen kusan kowanne dan Najeriya.Sai dai wadannan burace-burace, a galibin lokuta, ba sa cika – musamman ga masu matsakaitan samu.Amma wasu masana suna ganin akwai dabarun da marasa karfi ma za s...
•
24:47
Abin Da Ya Kamata Ku Yi Yayin Takaddama Da ’Yan Sanda
Babban alhakin da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya dora wa Rundunar ’Yan Sanda shi ne kare rayuka da dukiyoyin ’yan kasa. Sai dai a lokuta da dama, akan samu fito-na-fito sakamakon zargin ’yan sanda da wuce gona da iri wajen gudanar...
•
20:08