
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Episodes
798 episodes
Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi. Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da...
•
25:31

Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya
’Yan Najeriya suna ci gaba da nuna damuwa da yadda rahotannin kwace-kwacen waya suke karuwa a sassan daban-daban na kasa.Daya daga cikin rahotanni na baya-bayan nan shi ne inda a birnin Kaduna aka bayar da rahoton cewa wani matashi y...
•
24:02

Hanyoyin Fara Sana’a Ba Tare Da Jari Ba
Fara sana’a na cikin manyan jerin kalubalen da ’ƴan Najeriya suke fuskanta sakamakon wasu dalilai wadanda suka hada da rashin ilimi, ko Rashin wanda zai ba su shawara ko kuma, uwa uba, rashin jari.Wasu bayanai da Hukumar Ƙididdig...
•
25:18

Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah
Yau mutane na kallon bukukuwan Sallah da ido daban—yayin da wasu ke ganin ta zama lokaci na shakatawa nishadi kawai, wasu kuwa na cewa an bar al’adun da ke nuna kimar wannan babban lokaci na Musuluncin.Wadanda suka manyanta na ganin ...
•
27:10

Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma
Wata dabi’a da ta zama ruwar dare ita ce yadda matasa suke yankawa suke kuma da fige kaji a unguwanni, musamman a lokutan shagulgulan sallah.A da can akwai kebabbun wurare da ake gudanar da irin wadannan abubuwa.Sai dai masana su...
•
22:53

Hanyoyin Kauce Wa Barnar Ambaliyar Ruwa
Ambaliyar ruwa na ci gaba da raba dubban mutane tare da lalata dukiyoyi a fadin Najeriya. Ko a makon da ya gabata, wasu al’ummomi a Karamar Hukumar Mokwa dake Jihar Neja sun fuskanci irin wannan ambaliya da ta yi sanadiyyar rasa...
•
25:14

Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa
Shin wanne ya fi zafi – takaicin rasa matsuguni ko alhinin Rashin sanin halin da dan uwa na jini yake ciki?Wannan ne halin da wasu al’ummomi a Karamar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja suke ciki, bayan da suka tsinci kansu tsamo-tsamo a ts...
•
25:42

Yaya Girman Matsalar Rashin Tsaro A Shekaru Biyun Tinubu?
Rashin tsaro na cikin matsalolin da suke ci gaba da ci wa ’yan Najeriya da dama tuwo a kwarya, har a wannan lokaci da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yake cika shekara biyu a kan mulki.Wasu rahotanni da wasu kungiyoyi masu zaman kans...
•
25:41

Sai Yaushe ’Yan Najeriya Za Su Ci Gajiyar Manufofin Shugaba Tinubu?
A yau shekara biyu ke nan cif tun bayan da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi mulkin Najeriya a matsayin shugaban ƙasa na 16 tun bayan samun ‘yancin kai. Daya daga cikin abubuwan da shugaban kasar ya fara yi yayin ja...
•
27:39

Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
Najeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF).Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin wadannan yara suna fuskantar kalubale, kama daga cin...
•
25:29

Tasirin Dangantaka Tsakanin Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
A tsarin mulkin dimokuraɗiyya, dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisun dokoki tana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da shugabanci a tsakanin al’umma.A galibin kasashe masu bin tsarin na dimokuraɗiyya, ’yan majalisa kan k...
•
24:26

Dalilin ’Yan Adawar Najeriya Na Kulla Kawance A Karkashin Inuwar ADC
Mene ne ya sa jiga-jigan ’yan siyasar Najeriya bangaren adawa suka zabi inuwar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) don hada hannu da nufin kawar da Shugaban Kasa Bola Tinubu da APC dagga mulki?Da daren Talata ne dai jigogin a...
•
23:38

Illar Sare Itatuwa Ga Canjin Yanayi Da Lafiyar Mu
Shekaru da dama kenan da hukumomin duniya ke gudanar da tarurruka da dama kan zakulo hanyoyin da za a kawo karshen dumamar yanayi a duniya. Dumama ko canjin yanayi na cigaba da barazana ga duniya, inda ake samun sauye sauye ga yanayi d...
•
30:13

Yadda 'Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata. Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su. Sai d...
•
25:14

Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?
Daya daga cikin ginshikan tsarin dimokuradiyya shi ne zabi – bai wa jama’a dama su zabi abin da suke so, ko kuma wanda suke so ya shugabance su.Wannan ne ya sa daya daga cikin muhimman matakai a kafuwar tsarin shi ne zabe.Sai dai...
•
24:15

Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
Jam’iyyar NNPP wadda Dr. Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu karfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya. Shigowarsa...
•
24:24

Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Dalibai A Jarabawa
Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta yi amai ta lashe.Bayan ta musanta dukkan zarge-zargen da aka yi cewa tana da hannu a rashin kyawun sakamakon jarrabawar da ta shirya, Shugabanta ya fito ya amsa laifi.Yayi...
•
20:18

’Yan Najeriya Sun Yi Tir Da Biyan Diyya Ga Kwastomomin Rukunin Band A
Wasu ’yan Najeriya sun yi Allah-wadai da wani umarni da Hukumar da ke Kula da Harkar Wutar Lantarki a Najeriya, wato NERC, ta bai wa kamfanonin rarraba wutar lantarki da su biya diyya ga abokan huldarsu da ke rukunin Band A.Hukumar t...
•
15:59

Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Na GMO
Alamu na nuna cewa galibin manoma a Najeriya suna da shakku a kan amfani da irin da aka sauya ƙwayoyin halittarsa.Hakan dai na faruwa ne duk da bayanan da wasu masana suka yi game da alfanun wannan iri wanda ake kira GMO ko Ge...
•
25:25

Abun Da Yasa Muka Ƙasa Kawo Karshen Tamowa A Wasu Jihohin Arewa Maso Gabas
Hukumomi a jihar Yobe sun dora alhakin kazancewar matsalar tamowa a kan rikicin Boko Haram da rashin shayar da jarirai nonon uwa yadda ya kamata da kuma gurbacewar harkar kiwon lafiya, da sauran su.Bayanin hakan na zuwa ne bayan amba...
•
25:33

Kalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyan 'Ya'yan Su
Duk wanda ya shekara arbain zuwa sama ya san irin tarbiyyan da ya samo daga wurin iyayen sa a da baya can, irin mu’amalan dake tsakanin sa da iyaye har ma da shakuwan dake tsakanin ‘ya’ya da iyaye.A yanzu kuwa abubuwa sun canz...
•
27:12

Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?
Yin gwagwarmaya ko fafutuka wani abu ne da ke cikin jinin dan Adam, musamman idan yana kokarin ganin an samu sauyi ko cigaba a al'umma. Sai dai a Najeriya, sau da yawa ana danganta kalmar "gwagwarmaya" da rikici ko sabani da gwa...
•
27:16

Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka
A ko’ina a Nahiyar Afirka za a iya samun ɗan Najeriya da ya bar ƙasar sa domin rayuwa a wata ƙasa. A yau ba sai an je Turai ko Amurka ba – kasashe irin su Mali, Ghana, Libya, Sudan da sauran su suna cike da matasa ’yan Najeriya ...
•
29:01

Yadda Naira Biliyan Daya Ta Salwanta A Gobarar Kasuwar Jos
Kusan Naira biliyan day ace aka kiyasta ta salwanta sakamakon gobarar da ta kone wane sashe na babbar kasuwar dake tsakiyar Jos babbar birnin jihar Filato.An rawaito cewar gobarar ta lakume shaguna fiye da dari biyar, galibinsu na ma...
•
23:58
