Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Episodes
877 episodes
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
Cutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu ...
•
26:06
Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi. Hukumar kididdiga ta kasa ta f...
•
25:31
Ko Kawo Dakarun Kasar Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
Ana ta ce-ce- ku-ce kan batun da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi na kawo dakarun kasar sa Najeriya don taimakawa wajen yaki da matslar tsaro.Yayin da wasu ke ganin hakan abun san barka ne, wasu kuwa tofin Ala tsine su...
•
24:36
Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa. Wannan matsala ta daɗe tana jawo ...
•
24:31
Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya?
Tun bayan sauya hafsoshin tsaro da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ne dai mutane da dama keta tofa albarkacin bakinsu, yayin da wasu ke ganin hakan zai taimaka wajen yaki da rashin tsaro, wasu kuwa na ganin duk jama’ar ja ce.
•
25:03
Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas?
A cikin ‘yan watannin da suka gabata, an sake ganin karuwar hare-haren Boko Haram da ISWAP musamman a yankin Arewa maso Gabas. Kazalika, ko a kwanan nan ma anga irin wadannan hare hare.Wadannan hare-haren sun fi karkata kan sa...
•
27:08
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026
A ranar 26 ga watan Yuni, shekara ta 2025, gwamnatin tarayya ta sanya hannu kan sabon tsarin haraji wanda za a fara aiwatarwa daga ranar 1 ga Janairu, 2026. Wannan sabon tsarin haraji na daga cikin matakan da gwamnati ke ...
•
24:46
Halin Da Muka Shiga Sakamakon Haihuwar ‘Ya Mai Cutar Motsewar Kwakwalwa
Cutar Cerebral Palsy, wadda ake kira Ciwon tsukewar kwakwalwa, na daga cikin manyan matsalolin lafiyar yara da ke tasowa tun daga haihuwa. Wannan cuta tana faruwa ne sakamakon rauni ko lalacewar wani ɓangare na kwakwalwa da ke kula da motsi, ma...
•
28:46
Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?
Tun bayan fara shari’ar Nnamdi Kanu a shekarar 2021 mutane da dama suke bayyana ra’ayoyinsu a kan sake shi ko a kyale shari’a ta yi halinta.Hasali ma har zanga-zanga wasu ‘yan Najeriya suka kira don bayyana bukatar sakin shuga...
•
24:48
Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a
Cire darasin Lissafi daga jerin wajibcin da ake buƙata domin samun shiga manyan makarantu ya samu karɓuwa daga wasu ɓangarori na dalibai da malamai. Wasu dalibai sun nuna farin ciki da wannan mataki, suna ganin zai sauƙaƙa musu damar samun shig...
•
18:56
Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
Shekara da shekaru kungiyar malaman jami’oi ASUU ta kwashe ta na gudanar da yajin aiki ba tare da samun biyan bukata ba.Irin wannan yajin aiki da kungiyar malaman ke shiga ya jefa dalibai da malaman da ma harkar ilimi cikin ha...
•
23:07
Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Zabe Ta Kasa
A duk lokacin da a ka samu canjin shugabanci, hakan kan zo da kalubale da dama.Muƙamin shugabancin Hukumar Zabe ta kasa na daga cikin mukamai a Najeriya da 'yan kasa ke cece-kuce a kai.Ko wadanne irin Kalubale ne ke gab...
•
21:59
Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Nada Shugaban Hukumar Zabe
A tsarin mulkin Najeriya, an bai wa Shugaban Ƙasa ikon naɗa shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) tare da sauran mambobinta. Wannan iko yana daga cikin muhimman nauyukan da ke hannun shugaban ƙasa domin tabbatar da cewa ana gudan...
•
27:56
Tasirin Takardun Shaida Na Bogi Ga Rayuwar Al’umma
Takardun shaida na bogi na daya daga cikin matsaloli dake kara addabar Najeriya a fannoni da dama.A wasu lokuta ana samun mutane da ke amfani da takardun makaranta ko na ƙwarewa da ba su cancanta da su ba domin samun aiki, muk...
•
28:29
‘Halin Kunci Ya Sa Muke Zama A Baca A Abuja’
Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya.Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli....
•
27:20
Yadda Fasahar AI Ke Barazana Ga Sana’ar Masu Shagunan Daukar Hoto
A zamanin yau na fasahar zamani, musamman fasahar kirkirarriyar basir ta (AI), harkokin sana’o’i da dama suna fuskantar sauye-sauye masu girma. Daya daga cikin sana’o’in da ke cikin babban hadari shi ne sana’ar ɗaukar hoto musamman irin ...
•
22:56
Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Takarar Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan
Batun siyasar Najeriya ya sake ɗaukar hankali yayin da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, zai tsaya mata takarar shugaban ƙasa a 2027. Wannan batu ya tayar da muhawara mai zafi a tsakanin masan...
•
27:28
Me Ya Sa Mutane Suka Dawo Daga Rakiyar Kirifto?
A ’yan watanni da suka gabata, matasa da yawa a Najeriya sun dukufa don ganin hakar su ta cimma ruwa wajen samun kudaden kirifto.Amma alamu na cewa a baya-bayan nan wasu daga cikinsu sun sare sun kuma saduda sun dawo daga rakiyar harkar....
•
26:05
Hanyoyin Da Dangote, PENGASSAN Ba Su Bi Ba Don Magance Takaddamarsu
Gwamnatin Tarayya ta gayyaci Kungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) da Matatar Dangote don a sasanta a yau.Hakan ya biyo bayan umarnin da ’yan kwadagon suka bai wa mambobinsu ne na shiga yaji...
•
27:40
Hanyoyin Magance Gubar Cikin Abinci
Cin guba ta hanyar abinci (food poisoning) wata cuta ce da ke faruwa idan mutum ya ci abinci ko ya sha abin sha da ya gurɓace. Gurɓacewar abincin na iya fitowa daga ƙwayoyin cuta kamar Salmonella, E. coli, ko Listeria, ko kuma daga ƙwayoyin cut...
•
25:47
Dalilan Da Suke Sa Dalibai Cin NECO Fiye da WAEC
Yayin da dalibaI da dama da suka rubuta jarrabawar kammala karatun sakandare suka fitar da zaton samun gurbi a makarantun gaba a bana bisa la’akari da sakamakon WAEC, sai ga sakamakon NECO ya taho musu da sabon albishiri.Yayin da...
•
23:32
Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
Kisan jami’an tsaro na cigaba da zama ruwan dare a Najeriya, lamarin da ya daɗe yana tayar da hankali, amma a ‘yan kwanakin nan abin ya ƙara muni.Misali, kwanan nan a an kashe wasu jami’an ‘yan sanda a kananan hukumomin Katsin...
•
20:46
Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu
Wata cuta mai cin naman jikin dan’Adam ta yi sandin mutuwar mutum takwas yayin da wasu fiye da 60 suke kwance a asibiti a garin Malabu dake Karamar Hukumar Fufure ta Jihar Adamawa.Wannan lamari dai ya jefa fargaba a zukatan ma...
•
25:35
Ayyukan Da Fasahar AI Za Ta Raba Mutane Da Su Nan Ba Da Jimawa Ba
Mutane da dama na nuna damuwa game da mmakomar ayyukansu tun bayan fitowar fasahar AI.Sai dai yayin da wasu manazarta suke ganin fasahar za ta raba mutane da ayyukansu, wasu kuwa gani suke yi wannan ba abu ne mai yiwuwa ba.<...
•
20:13
Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?
A yau ne Gwamna Siminalaye Fubara ke dawowa kujerarsa a matsayin gwamnan Jihar Ribas bayan dakatarwa da ayyana dokar ta baci na watanni shidda da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi a jihar.Manazarta dai na hasashen wannan d...
•
25:13