Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Shekara 23 Da Mulkin Dimokuradiyya; Ina Aka Kwana?
•
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed
Ranar 12 ga Yuni na 2022 mulkin dimokuradiyya ke cika shekara 23 da kafuwa a Najeriya ba tare da samun wani cikas ba.
A wadannan shekaru idan an saka kasar a fai-fai, cigaba aka yi ko kuma baya, mene ne ake bukatar a gyara a tafiyar da dimukuradiyya Najeriya.
'Yan Najeriya sun tofa albarkacin bakinsu kan yadda su ke kallon yanayin mulkin a Najeriya, sannan mun tuntubi masana domin sanin abinda ya kamata a gyara a tafiyar mulkin kasar.