Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Yadda Aka Yi Cinikin Kuri’a A Zaben Ekiti
•
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed
Rahotanni daga Jihar Ekiti inda aka gudanar da zaben gwamna a ranar Asabar sun bayyana zargin sayen kuri’a.
Mun tattauna da jama’a daga jihar ta Ekiti kan gaskiyar abin da ya faru, mun kuma tuntubi masana shari’a kan matsayin mai sayen kuri’a da mai sayarwa da kuma wanda aka saya domin sa.
A yi sauraro lafiya.