Najeriya a Yau

Dalilin Da 'Yan Boko Haram Ke Yanka 'Yan Jari Bola A Maiduguri

June 21, 2022 Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed
Najeriya a Yau
Dalilin Da 'Yan Boko Haram Ke Yanka 'Yan Jari Bola A Maiduguri
Show Notes

A 'yan kwanakin nan rahotanni sun bayyana cewa 'yan boko haram sun yanka 'yan jari bola sama da 50 a kasa da kwana 30 a Jihar Borno.

Irin wannan hari dai ba kasafai ake samun irinsa ba. Ko me ya janwo hakan?

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya tattauna da masu ruwa da tsaki daga Jihar Borno kan yadda abin ya kasance, wadanda aka kashe da kuma dalilin makasan.