Najeriya a Yau

Dalilan Da Ake Yi Wa Mutum Kutse A Soshiyal Midiya

Muhammad Auwal Sulaiman, Muslim Muhammad Yusuf, Nana Khadija Ibrahim

Send us a text

Masu amfani da shafukan sada zumunta kan fada hannun masu dandantsa inda sukan yi kutse a shafin mutum har ya rasa iko da shi.

Kwararru sun ce ana yi wa wasu hakan domin bata suna ko kuma neman kudi da damfara.

Shirin Najeriya a Yau ya tattauna da kwararru a fannin samar da matakan tsaro a soshiyal midiya game da dabarun inganta tsaron shafukanku.