
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Guraben Aiki Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya
•
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim
Duk da kukan rashin aikin yi da ako da yaushe ke cigaba da addabar ‘yan Najeriya, a wasu lokutan ba rashin aikin yi ne matsalar ba, wadanda zasu cike guraben ayyukan ne suka yi karanci a Najeriya.
Alkaluma na cigaba da bayyana dubban ‘yan Najeriya ne dai ke fito wa daga manyan makarantun kasar a kowace shekara.
A yayin da da yawa basa samun aikin yi, so tari akwai dimbin guraben ayyuka da babu masu cike su don babu kwararrun da ake bukata.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai tattauna ne kan guraben ayyukan da aka kasa cike su da kuma nemo hanyoyi don magance matsalar.