
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Kasa Kiranye
Mulkin demokradiyya kamar yadda Hausawa ke cewa ‘yancin dan adam.
A lokacin da ta baka damar tsayawa don a zabe ka kan wani mukami, kazalika ta baka damar zaben wanda kake so ya shugabance ka kuma ya wakilce ka.
Wani abun da demokradiyyar ta baiwa alumma dama a kai kuma shine na yin kiranye ga wakilan da suka zaba musamman idan wadannan wakilan basa biya musu bukatun da suka tura su a kai.
Tuni dai alummar kogi ta tsakiya suka fara kada kuri’un kiranye ga sanatar da suka aike ga majalisar dattawa bisa dalilai nasu na kashin kan su.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai tattauna ne kan matakai da sharuddan da ake cikawa don yin kiranye ga ‘yan majalisa.