
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
•
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim
Alqurani mai girma a cikin suratul Baqarah Allah ya wajabta wa musulmi da suka cika wasu sharudda azumtar watan Ramadana.
Kamar yadda malamai suka sha fadi, wannan wata na dauke da wasu falala maras misaltuwa da bawa kan samu idan ya maida kai wajen ibada don samun rabauta daga ubangiji.
Kazalika hadisai sun ruwaito kan falalar azumtar kwanaki shidda na watan shawwal, watan dake biye da Ramadan.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan falalar dake akwai ga wanda ya azumci kwanaki shidda na watan shawwal.