
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Dalilan Rikice – Rikice A Jihar Filato
•
Idris Ɗaiyab Bature
A yanzu haka, al’ummar jihar Filato na cikin fargaba da tashin hankali sakamakon jerin hare-haren da suka afku a wasu sassan jihar, inda daruruwan mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka tsere daga muhallansu.
Ko mene ne dalilin sake fitowar rikice-rikicen da suka dabaibaye yankin da ake ganin an fara samun zaman lafiya?
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan rikice rikicen Jihar Filato da dalilan aukuwar su.