Najeriya a Yau

Dalilan Rikice – Rikice A Jihar Filato

Idris Ɗaiyab Bature

Send us a text

A yanzu haka, al’ummar jihar Filato na cikin fargaba da tashin hankali sakamakon jerin hare-haren da suka afku a wasu sassan jihar, inda daruruwan mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka tsere daga muhallansu.


Ko mene ne dalilin sake fitowar rikice-rikicen da suka dabaibaye yankin da ake ganin an fara samun zaman lafiya?


Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan rikice rikicen Jihar Filato da dalilan aukuwar su.