
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Matakan Dakile Kisan Matafiya A Hanyoyin Kasar Nan
•
Idris Ɗaiyab Bature
Matsalar tare fasinjoji da kashe su a hanyoyin Najeriya na kara tsananta, musamman a yankunan Arewa.
Misali, a shekarun baya an sha tare matafiya tare da kashe wasu daga cikin su a hanyar Abuja zuwa Kano, a kwanakin baya ma an kashe wasu matafiya a garin Uromi dake jihar Edo a hanyar su ta komawa gida, sai na kwanan nan da ya faru a jihar Filato inda aka kashe wasu matafiya dake kan hanyar su na zuwa daurin aure.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne da nufin gano matakan dakile afkuwar haka a nan gaba.