
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Halin Da Alummar Mokwa Ke Ciki Wata Guda Bayan Ambaliya
•
Idris Daiyab Bature
Tun bayan da ambaliyan ruwa ya ci wasu sassan garin Mokwa ne dai alummar garin suka fada halin neman taimako.
A yayin da gwamnatin tarayya da ma wasu daidakun mutane suka taimaka ma wadanda abun ya shafa da kudi da ma wasu kayayyakin masarufi, wasu daga cikin alummar sun bayyana rashin jin dadin su ga yadda alamura ke gudana a garin Mokwa.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai nazari ne kan halin da alummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliyar ruwan da ci wasu sassan na garin.