
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Boyayyun Kalubalen Da Sabuwar Hadakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
•
Idris Daiyab Bature
Tun kafin sanar da sabuwar kawance da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yiwa wannan hadaka zagon kasa da kawo cikas ga tafiyar wannan hadaka.
Daya daga cikin irin wadannan zagon kasa da ake zargin wasu da yiwa wannan sabuwar hadaka itace na sanar dasu rashin samun dakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci kalilan gabanin taron.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan boyayyun kalubalen da sabon hadakar jamiyyar ADC zata iya fuskanta gabanin 2027.