
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Abin da ya sa muke yi wa PDP zagon ƙasa — Sule Lamiɗo
•
Idris Daiyab Bature
Zagon kasa da wasu ‘ya’yan PDP ke yi mata na kara ta’azzara, inda wasu ke zama a cikin ta amma suke wa jam’iyyun adawa aiki.
Ko a kwanan nan, an hangi wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar a taron hadakar ADC, wadda hakan ke jaddada har yanzu PDP ta kasa kawo karshen wannan matsala.
Ko me yasa ‘ya’yan PDP ke yiwa jam’iyyun adawa aiki?
Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.