Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Dalilan Karuwar Mace-Mace A Hanyoyin Najeriya
Use Left/Right to seek, Home/End to jump to start or end. Hold shift to jump forward or backward.
Duk da kara wayar da direbobi da fasinjoji da hukumar kiyaye hadura ta tace tana yi, ana kara samun hauhawar wadanda ke rasa rayukansu sakamakon haddura a titin kasar nan.
A shafinta na internet, hukumar kiyaye haddura ta kasa tace a watanni uku na farko na shekarar 2024, mutane 1,471 ne suka rasa rayukansu sakamakon hatsarin mota, kazalika, a watanni uku na farko na wannan shekara ta 2025, adadin ya haura zuwa mutane 1,593 — karin mutum 122, ko kuma kashi 8.3 cikin dari.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ake kara samun karuwa rasa rayuka a titunan kasar nan.