Najeriya a Yau

Dalilan Karuwar Mace-Mace A Hanyoyin Najeriya

Idris Daiyab Bature

Use Left/Right to seek, Home/End to jump to start or end. Hold shift to jump forward or backward.

0:00 | 25:50

Send us Fan Mail

Duk da kara wayar da direbobi da fasinjoji da hukumar kiyaye hadura ta tace tana yi, ana kara samun hauhawar wadanda ke rasa rayukansu sakamakon haddura a titin kasar nan.


A shafinta na internet, hukumar kiyaye haddura ta kasa tace a watanni uku na farko na shekarar 2024, mutane 1,471 ne suka rasa rayukansu sakamakon hatsarin mota, kazalika, a watanni uku na farko na wannan shekara ta 2025, adadin ya haura zuwa mutane 1,593 — karin mutum 122, ko kuma kashi 8.3 cikin dari.


Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ake kara samun karuwa rasa rayuka a titunan kasar nan.