
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Tasirin Takaddamar NUPENG Da Dangote A Kan Tattalin Arzikin Najeriya
•
Idris Daiyab Bature
’Yan Najeriya sun shiga taraddadin abin da ka iya biyo bayana kudurin Kungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (NPENG) na tsunduma yajin aiki.
Hakan dai ya biyo bayan tashi da aka yi daga zaman da Gwamnatin Tarayya ta kira don sasanta kungiyar, mai samun goyon bayan sauran kungiyoyin kwadago, da rukunin kamfanonin Dangote, ba tare da cimma wata matsaya ba.
Ministan Kwadago Muhammadu Dingyadi ne dai ya kira taron, wanda ya samu halartar jami’an gwamnati da wakilan kungiyoyin NUPENG da NLC da TUC da na Dangote da kuma MRS, da nufin hana yajin aikin.