Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Hanyoyin Da Dangote, PENGASSAN Ba Su Bi Ba Don Magance Takaddamarsu
•
Idris Daiyab Bature
Gwamnatin Tarayya ta gayyaci Kungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) da Matatar Dangote don a sasanta a yau.
Hakan ya biyo bayan umarnin da ’yan kwadagon suka bai wa mambobinsu ne na shiga yajin aiki bayan da Matatar Dangote ta salami ma’aikata fiye da 800.
Sai dai wasu masana suna ganin tun farko bai kamata lamarin ya kai ga haka ba da an bi wasu hanyoyi.
Wadannan hanyoyi shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai binciko.