Najeriya a Yau

‘Halin Kunci Ya Sa Muke Zama A Baca A Abuja’

Idris Daiyab Bature

Send us a text

Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya.


Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli.

Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi?


Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.