Najeriya a Yau

Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Ta

Idris Daiyab Bature

Send us a text

Cutar kansar mama na ɗaya daga cikin manyan cututtukan da ke addabar mata a Najeriya da ma duniya baki ɗaya. 


An kiyasta cewa mata sama da dubu ɗari biyu na kamuwa da cutar a kowace shekara a Najeriya, yayin da miliyoyin mata a duniya ke fama da wannan cuta. Abin damuwa shi ne cewa yawancin lokuta ana gano cutar ne a kurarren lokaci, wanda hakan ke sa magani ya yi wahala kuma ya rage yiwuwar ceto rayuwar wanda ya kamu da shi.


Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.