Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Siyasa Da Tsare-tsaren Gwamnati Da Suka Dabaibaye 2025
Use Left/Right to seek, Home/End to jump to start or end. Hold shift to jump forward or backward.
Yayin da muke bankwana da shekarar 2025, siyasar Najeriya ta kasance cike da sauye-sauye, rikice-rikice, da kuma manyan al’amura da suka shafi iko, jam’iyyu da shugabanci. Shekarar ta shaida sauyin sheƙa na ‘yan siyasa, rikicin cikin gida a wasu jam’iyyu, da kuma fafutukar karɓar ragamar mulki a jihohi da matakin tarayya, lamarin da ya ƙara zafafa siyasar ƙasa.
A bangaren tsare-tsaren gwamnati kuwa, 2025 ta kasance shekara mai ɗauke da tsauraran manufofi da suka shafi tattalin arziki, tsaro da walwalar al’umma. Gwamnati ta ɗauki matakai masu nauyi domin tinkarar matsalolin tsadar rayuwa, rashin tsaro da sauye-sauyen tattalin arziki, inda wasu tsare-tsaren suka samu karɓuwa, wasu kuma suka jawo muhawara mai zafi a tsakanin ‘yan kasa.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya yi waiwaye ne kan siyasa da tsare-tsaren gwamnati da suka dabaibaye shekarar 2025 da muke bankawana da ita.