Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Yadda ‘Yan Bindiga Suka Yanka ‘Yan Kasuwa A Jihar Neja
Use Left/Right to seek, Home/End to jump to start or end. Hold shift to jump forward or backward.
Harin da wasu ‘yan ta’adda suka kai kasuwar Daji da ke karamar hukumar Borgu a Jihar Neja ya sake jawo hankalin al’umma kan matsalar rashin tsaro da ke kara ta’azzara a yankunan karkara na Arewa ta Tsakiya. Kasuwar Daji, wadda ke zama cibiyar hada-hadar kasuwanci ga manoma, ‘yan kasuwa da mazauna kauyuka makwabta, ta kasance wuri na zaman lafiya kafin wannan mummunan lamari da ya girgiza mazauna yankin.
Batutuwa da dama daga kafafen yada labarai da dama sun bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan batun.
Ko menene hakikanin abun da ya faru a wannan hari da ‘yan bindiga suka kai a kasuwar Daji?
Wannan shine batun da shirin Najeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba akai.